Connect with us

ilimi

Gwamnatin Tarayya ta amince da sabbin jami’o’i 9

Published

on

Gwamnatin tarayya ta amince da kafa sabbin jami’o’i masu zaman kansu guda tara.

Ministan Ilimi, Dakta Tunji Alausa, ne ya sanar da hakan a jiya  Laraba, yayin da yake zantawa da manema labarai a fadar shugaban ƙasa, bayan taron majalisar zartarswa ta ƙasa da shugaba Bola Tinubu ya jagoranta a birnin tarayya Abuja.

Ya ce, jami’o’in da aka amince da su sun haɗa da:

Jami’ar Tazkiyah da ke jihar Kaduna

Jami’ar Leadership da ke babbar birinin tarayya, Abuja

Jami’ar Jimoh Babalola a jihar Kwara

Jami’ar Bridget, Mbaise a jihar Imo

Jami’ar Greenland da ke jihar Jigawa

Jami’ar JEFAP a jihar Neja

Jami’ar Azione Verde da ke jihar Imo

Jami’ar Unique Open a Jihar Legas

Jami’ar American Open da ke Jihar Ogun

A cewar Ministan  gwamnatin Tinubu ta gaji buƙatu 551 na kafa sababbin jami’o’i, inda aka saka tsauraran ka’idojin tantancewa kafin amincewa da su.

Alausa ya ce  da dama daga cikin jami’o’in da aka amince da su suna jiran samun izinin aiki sama da shekaru shida, duk da cewa masu hannun jari sun riga sun gina harabar makaranta tare da zuba biliyoyin naira a ciki.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!