Connect with us

Labarai

Gwamnatin Tarayya ta ce ƙasashe 65 sun amince da karɓar jakadun Najeriya

Published

on

Gwamnatin Tarayya ta ce ƙasashe 65 daga cikin 69 da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya naɗa wa jakadu sun amince da karɓar su, abin da ya kai kashi 97 cikin 100 na dukkan nade-naden.

Ma’aikatar Harkokin Wajen Najeriya ta bayyana cewa ƙasashe biyu ne kaɗai suka rage ba su kammala bayar da amincewarsu (agrément) ga jakadun da aka tura musu ba.

A cewar ma’aikatar, jakadan da aka nufa da tura shi ƙasar Togo ya ƙi karɓar nadin, yayin da jakadan da aka tura Aljeriya ya rasu a watan Afrilun 2026.

Sanarwar ta ƙara da cewa yawancin jakadun da aka naɗa sun riga sun isa ƙasashen da aka tura su, inda suka gabatar da takardun shaidar aikinsu ga shugabannin ƙasashen da za su yi aiki, tare da fara gudanar da ayyukansu na wakiltar Najeriya.

Tun a watan Maris na 2026 ne Shugaba Tinubu ya amince da tura jakadu 69 zuwa ƙasashe daban-daban da kuma ofisoshin Majalisar Ɗinkin Duniya, bayan Majalisar Dattawa ta tabbatar da su.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!