Labarai
Gwamnan Kogi Ahmed Usman Ododo ya yaye jami’an tsaron dazuka 530

Gwamnan Jihar Kogi, Ahmed Usman Ododo, ya yaye jami’an tsaron dazuka 530.
Wannan na cikin sanarwar da Kwamishinan Yaɗa Labaran Jihar, Kingsley Femi Fanwo, ya fitar a jiya Asabar
Sanarwar ta ce an gudanar da bikin yaye rukuni na farko na jami’an tsaron dazuka a Muhammadu Buhari Civic Centre da ke Lokoja.
Ya ce mutane 539 ne suka fara horaswar ta makonni takwas, inda 530 suka kammala domin fara aiki.
Sanarwar ta ce gwamnan ya sake jaddada aniyar gwamnatinsa ta ci gaba da samar da kayan aiki da tallafin da ake buƙata domin ƙarfafa hukumomin tsaro, tare da kira ga mazauna jihar su riƙa ba jami’an tsaro sahihan bayanan da za su taimaka wajen inganta tsaro.
You must be logged in to post a comment Login