Connect with us

Labarai

Kwamitin yaƙi da faɗan daba da miyagun ƙwayoyi ya kai samame wasu wurare

Published

on

Kwamitin karta-kwana na yaƙi da faɗan daba da ta’ammali da miyagun ƙwayoyi na Jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin shugabansa, Barista Muhyi Magaji Rimin Gado, ya kai ziyarar duba wasu manyan wuraren da ake zargin ana gudanar da hada-hadar miyagun ƙwayoyi a cikin Birnin Kano.

Wuraren da kwamitin ya ziyarta sun haɗa da Rekwa, Filin Mahaha, Ɗan’agundi, Kwarin Dala da kuma Filin Sabuwar Kofa.

Ziyarar na daga cikin matakan da kwamitin ke ɗauka domin ƙara sa ido tare da ƙarfafa yaƙi da masu ta’ammali da safarar miyagun ƙwayoyi, da kuma magance matsalar faɗan daba da sauran ayyukan da ke barazana ga tsaro a faɗin jihar.

Da yake ƙarin bayani ga Freedom Radio, shugaban kwamitin, Barista Muhyi Magaji Rimin Gado, ya ce sun fara samun nasarori a ƙoƙarin da suke yi, yana mai jaddada cewa kwamitin zai ci gaba da irin waɗannan ziyarce-ziyarcen domin tabbatar da zaman lafiya da kare rayuka da dukiyoyin al’ummar Jihar Kano.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!