Connect with us

Labarai

Gwamnatin tarayya ta ce tana dab da kammala aikin Solar a Asibitin koyarwa na Malam Aminu Kano

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ce nan da watanni uku masu zuwa za ta kammala aikin wuta mai amfani da hasken rana a Asibitin koyarwa na Malam Aminu Kano domin tsayar musu da wuta ta tsawon awanni ashirin da hudu ba tare da ɗaukewa ba, domin kulawa da lafiyar al’umma.

Shugaban hukumar makamashi na ƙasar nan Dakta Abdullahi Mustapha ne ya bayyana hakan a yau yayin ƙaddamar da fara aikin wutar mai anfani da hasken rana a asibitin koyarwa na Malam Aminu kano wanda shugaban kwamitin shirye shiryen kasafin kuɗi na majalisar tarayya kuma ɗan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Bichi Abubakar Kabir Bichi ya samar.

A nasa jawabin shugaban kwamitin shirye shiryen kasafin kuɗi na majalisar tarayya kuma ɗan majalisa mai wakiltar Bichi Abubakar Kabir Bichi da ya assasa aikin yace ganin irin halin da asibitin yake ciki ya sanya shi wannan yunkuri na samar da kudi sama da biliyan sha shida domin samar musu da tsayayyiyar wuta a cikin asibitin.

Shugaban Asibitin na Malam Aminu Kano Farfesa Abdulrahman Abba Sheshe, a jawabin sa cikin harshen turanci ya godewa gwamnatin tarayya bisa yunkurin samar da wutar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!