Connect with us

Labarai

Gwamnatin tarayya ta duƙufa wajen magance matsalolin tsaro- Ministan yaɗa Labarai

Published

on

Gwamnatin tarayya ta bakin  ministan yaɗa labarai da wayar da kan jama’a Modammed Idris, ta ce, ta duƙufa wajen magance matsalolin tsaron da ƙasar ke fuskanta, ta yadda ƴan ƙasar dama baƙi ƴan ƙasashen ketare  za su kasance cikin tsaro a kowane yanki suke.

Jawabin Ministan, ya biyo bayan gargadin Ofishin kula da harkokin ƙasashe renon Ingila na Commonwealth  da ya ce su guji yin balaguro zuwa jihohin Borno da Yobe da Adamawa da Gombe da Katsina da kuma Zamfara, saboda ƙaruwar tashe-tashen hankali da ta’addanci da kuma garkuwa da mutane.

A nata ɓangaren, gwamnatin jihar Kano ta bakin sakataren yaɗa labaran gwamnan jihar Mustapha Muhammad, ta ce al’umma su ci gaba da gudanar da harkokinsu yadda suka saba, domin babu wata barzana kan wancan gargaɗi na gwamnatin Birtaniyya.

Haka nan itama gwamnatin jihar Borno, ta ce an samu gagarumar nasara wajen inganta lamuran tsaro a cikinta, da mai taimawa gwamna Babagana Zulum kan harkokin tsaro Janar Abdullahi Ishaq mai ritaya, ya ce ba za su ce komai game da kiran na Birtaniyya ba, gwamnatin tarayya ce za ta maida martani akai.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!