Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatin tarayya ta sanar da sabbin ka’idojin bude makarantu

Published

on

Yayin da dama daga makarantun kasar nan za su bude a ranar litinin na makon gobe, gwamnatin tarayya ta kara fitar da wasu sabbin ka’idoji da ta zayyanawa makarantu domin kare dalibai daga kamuwa da cutar corona.

Cibiyar dakile yaduwar cututtuka ta kasa NCDC ce ta bayyana haka yayin zantawa da jaridar PUNCH.

A cewar cibiyar ta NCDC wajibi ne makarantun su rika auna hatsarin da cutar corona ke da shi a duk mako don rage hatsarin da dalibai da malamai za su shiga.

Haka zalika an kuma bukaci jihohi da kananan hukumomi da su rika nazartar halin da cutar ke ciki a duk wata ko bayan watanni hudu-hudu.

Shugaban cibiyar dakile yaduwar cututtuka ta kasar Dr Chikwe Ihekweazu ya shaidawa jaridar cewa, wadannan mataki wajibi ne makarantu su rika daukarsu don kare lafiyar dalibai da malamai.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!