Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kafin bude makarantu gwamnati ta kare dalibai daga corona -Majalisar dinkin duniya

Published

on

Majalisar dinkin duniya ta shawarci gwamnatin tarayya da ta tabbatar da cewa ta dauki matakan da suka kamata don kare dalibai daga kamuwa da cutar corona, kafin bude makarantun kasar nan.

Majalisar ta kuma ce a kalla daliban firamare da na sakandire sama da miliyan arba’in da shida ne a Najeriya ke cikin hatsarin kamuwa da cutar corona, idan ba a dauki matakan kariya ba, bayan bude makarantun.

Hakan na cikin wata sanarwa ce mai dauke da sa hannun babban jami’in majalisar dinkin duniya a Najeriya, Mista Edward Kallon.

Mista Edward Kallon, ya kuma ce, bai wa dalibai kariya shi ne abu mafi mahimmanci da ya kamata gwamnatoci su mayar da hankali don tabbatar da an kare lafiyar su a yayin neman ilimi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!