Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatocin jihohi ne za su rinka ciyar da daurarru- Minista

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ce, daga yanzu gwamnatocin jihohi ne za su rika ciyar da fursunoni da ke gidajen ajiya da gyaran hali.

Ministan harkokin cikin gida Rauf Aregbesola ne ya sanar da hakan, lokacin da yake jawabi a wajen wani babban taro na kwanaki 2 kan rage cunkoson Fursunoni a gidajen gyaran hali da aka gudanar a Birnin tarayya Abuja.

Ya ce, ‘hakan ya biyo bayan gyare-gyaren da aka yi wa kundin tsarin mulkin kasar nan a baya-bayan nan wanda Ya nuna cewa, a yanzu an baiwa jihohi ikon ciyar da fursunonin da ke daure’.

Aregbisola ya kuma ce, ‘duk jihar da ta gaza ciyar da fursunoninta, to kuwa dole ne ta biya gwamnatin tarayya kudin ciyarwar’.

Idan za a iya tunawa, a baya gwamnatin tarayya ta ware sama da naira biliyan 22 domin ciyar da fursunoni a dukkanin gidajen gyaran hali guda 244 da ke fadin Nigeriya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!