Connect with us

Ƙetare

Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ta sake sanya dokoki masu tsauri ga yan Najeriya

Published

on

Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa, UAE ta sake saka wasu dokoki masu tsauri ga ‘yan kasar nan da ke neman bizar shiga ƙasarta domin yawon buɗe ido ko ziyarar wucin-gadi.

 

Sanarwar da ƙasar ta fitar ta haramta bai wa ‘yan Najeriya bizar wucin-gadi, kuma ɗuk wani ɗan Najeriya mai shekaru 18 zuwa 45 ba za a ba shi bizar shiga ƙasar ba, sai tafiyar ta kasance da iyali.

 

Sabon matakin  na zuwa ne kusan shekara ɗaya da UAE da Najeriya suka shawo kan matsalar haramcin bizar na shekara biyu da aka kakabawa ‘yan Najeriyar.

 

A yanzu dai wannan sabon doka na nufin an soke ba wa ‘yan Najeriya bizar wucin-gadi baki daya haka zalika  ga wanda ya haura shekara 45 idan yana neman biza sai ya gabatar da takardar bayanan asusun ajiyar sa na banki na tsawon wata shida, wanda zai nuna yana da kuɗaɗen da suka kai dala dubu 10 a lokacin neman bizar.

 

Sai kuma bukatar gabatar da Otel din da mutum zai yi masauki da kuma wasu bayanai na fasfo.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!