Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Haɗin kan al’umma ne ke samar da ƙasa ɗaya dunƙulalliya – Dakta Sa’idu Dukawa

Published

on

Shugaban sashin nazarin harkokin mulki da gudanarwa a jami’ar Bayero kuma masanin kimiyyar siyasa a nan Kano ya ce, ƙasa ɗaya dunƙulalliya na samuwa ta hanyar haɗin kan al’ummar da ke rayuwa a cikin ta.

Dakta Sa’’idu Ahmad Dukawa ne ya bayyana hakan a zantawar sa da Freedom Radio.

Dukawa ya ce “Kasa a siyasance na nufin wani guri da al’umma da yawa ke zaune kuma yaruka daban-daban ɗabi’unsu daban, al’adunsu daban, amma suna zaune tare kuma suna rayuwa tare cikin kwanciyar hankali”.

“Gwamnati ita ce akan gaba wajen haɗa kan ƙasa, ta hanyar samarwa da al’ummar da ta ke mulka ilimi, lafiya da kuma yin adalci” in ji Dukawa.

Masanin ya kuma ce, in dai ana so ƙasa ta zama ɗaya dunƙulalliya to kuwa sai shugaban da ya ke jagorantar ta ya sauke nauyin da ke kan sa.

Da kuma tuna cewa al’ummar su ne suka zaɓe shi don ya jagorance su.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!