Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Hukumar DSS ta musanta cewa jami’anta na da hannu wajen taimakawa Nnamdi Kanu wajen tserewa

Published

on

Hukumar tsaron sirri ta DSS ta musanta cewa wasu jami’anta guda biyar suna da hannu wajen taimakawa shugaban ‘yan awaren Biafra ta IPOB Nnamdi Kanu tserewa daga gidansa da ke garin Umuahia a jihar Abia a ranar 14 ga watan Satumban shekarar da ta gabata.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun jami’in yada labaran hukumar Peter Afunanya.

Sanarwar ta ce labaran da yak e bayyana cewa wasu jami’in hukumar biyar ne suka tallafawa Nnamdi Kanu tserewa shifcin gizo ne kawai.

Hukumar ta DSS ta kuma bayyana cewa manufar wadanda suka yada farfagandan shine domin bata sunan hukumar.

Mr. Peter Afunanya ya kara da cewa masu yada farfagandan suna kuma yunkurin kawo matsala ga babban zaben kasa wanda za ayi a shekarar badi.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!