Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Hukumar EFCC tayi wa tsohuwar ministan sufurin jiragen sama tambayoyi

Published

on

Jami’an Hukumar EFCC mai yaki da cin hanci da rashawa sun yi wa tsohuwar Ministar Sufurin jiragen saman kasar nan Stella Oduah tambayoyi bayan gurfana da ta yi a Ofishin hukumar a jiya.

Stella Oduah ta shafe tsawon Sa’o’i takwas tana amsa tambayoyi kan wani kwantiragin sama da Naira Biliyan 9 da ta baiwa wani Kamfani domin samar da kayayyakin tsaro a Filayen Jiragen sama 22 a fadin kasar nan.

Wakilan wani kamfanin kasar Amurka da EFCC ta gayyata domin bada ba’asi, ya shaida cewa Misis Stella Oduah ta kwace kwangilar dag hannunsu sannan ta mikawa wani kamfani da take da alaka da shi.

Rahotanni sun nuna cewa EFCC ta aikewa Stella Oduah takardar gayyata tun a ranar 13 ga watan Yunin bara amma ta ki mutunta gayyatar har sai da ta ji labarin suna kokarin ayyana ta a matsayin wadda suke nema ruwa a jallo, sannan ta gurfana a jiya.

Stella Oduah dai ita ce ’yar Majalisar Dattijai mai wakiltar Anambra ta Arewa.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!