Labarai
Hukumar FRSC ta yi wa manyan jami’anta 162 sauyin wuraren aiki

Hukumar kiyaye afkuwar hadura ta kasa FRSC ta amince da sauya wurin aiki ga manyan jami’anta 162 a wani babban sauyi da aka yi a manyan mukaman hukumar.
Hukumar ta bayyana haka ne ta cikin wata sanarwa da mataimakin kwamandanta mai kula da harkokin gudanarwa, Agboola Olundegun, ya fitar yau Alhamis a Abuja.
sanarwar, ta ruwaito cewa, shugaban hukumar Malam Shehu Mohammed, ne ya amince da wadannan sauye-sauye, inda ya bayyana cewa an yi hakan ne domin karfafa ayyuka da kuma inganta ayyukan hukumar na kare afkuwar haduna a fadin kasar nan.
Haka kuma, ya kara da cewa, wannan tsarin ya hada da nadin sabbin kwamandojin yankuna guda hudu da kuma sauya wurin aiki ga kwamandojin sassa zuwa wasu jihohi da sassan da dama
Shugaban hukumar ya kuma amince da nadin sabon shugaban sashen wayar da kan jama’a, inda aka daga mukamin tsohon mataimakin shugaban sashen, Osondu Ohaeri, domin jagorantar harkokin sadarwa da fadakar da jama’a na hukumar.
You must be logged in to post a comment Login