Connect with us

Labarai

Hukumar gidajen gyran hali ta Kano ta musanta zargin yin lalata da matasa

Published

on

Hukumar kula da gidajen gyran hali da tarbiya  ta Najeriya shiyyar Kano, ta musanta wani rahoto da ya bayyana cewa ana yin lalata da matasan da ke tsare a gidan gyran hali na Goron Dutse kamar yadda wani matashi ya bayyana.

A makon da ya gabata ne matashi wanda ya ce ya  zauna a gidan gyaran halin na Goron Dutse mai suna Shehu Adamu ya  zargi hukumar gidan da yin sakacin da ya janyo ake yin lalata da daurarrun.

Sai dai ta cikin wata sanarwa da ya fitar kan batun, jami’in hulda da jama’a na hukumar lura da gidajen gyran hali na Kano DSC Musbahu Lawal Kofar Nasarawa, ya karyata maganganun matasan.

DSC Musbahu Lawal, ya kara da cewa hukumar gidan gyaran halin ta Kano za ta dauki matakin shari’a a kan matashin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!