Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Hukumar gudanarwar customs ta yi karin girma ga manyan jami’an ta 1997

Published

on

Hukumar gudanarwar hukumar kwastam ta yi karin girma ga wasu manyan jami’an hukumar 1997.

Haka kuma ta kuma amince wasu manyan jami’an na kwastam hudu su kasance cikin hukumar gudanarwar.

Karin girma ga manyan jam’ian ya faru ne yayin wani taro da hukumar gudanarwar ta gudanar wadda shugaban ta ministan kudi Kemi Adeosun ta jagoranta.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar Mr Joseph Attah ya fitar jiya a Abuja.

A cewar sanarwar, karin girmar ya fara aiki ne tun a ranar daya ga watan Janairun shekarar da ta wuce.

Wasu daga cikin manyan jami’an hukumar ta kwastam da aka yi wa karin girmar sun hada da: DCS Talatu Isa Mairo da ACG Ibrahim Yakubu Maikarfi da ACG Ali Bukari Ama Amajam da kuma Comptroller Adesanmi Omiye.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!