Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Hukumar Kwastam tayi karin girma ga jami’anta

Published

on

Hukumar yaki da fasakwauri ta kasa kwastam ta yi karin girma ga wasu jami’nta guda dubu daya da dari tara da ashirin da hudu.

Mai magana da yawun hukumar Joseph Attah ne ya bayyana haka ga manema labarai ta cikin wata sanarwa da ya fitar jiya a Abuja.

Sanarwar ta ce, hamsin da daya daga ciki mataimakan sufeton kwastam ne wadanda aka yi musu karin girm zuwa sufeto haka kuma wasu masu mukaman na AIC arba’in da takwas an daga likkafar su zuwa IC.

A cikin sanarwar mai magana da yawun hukumar Joseph Attah ya ce karin girmar ya fara aiki ne nan take.

Haka zalika sanarwar ta ruwaito shugaban hukumar ta kwastam kanal Hamid Ali mai ritaya na yin kira ga wadanda aka yi wa karin girmar da su rubanya kokarin su wajen dakile ayyukan fasakwauri a kasar nan.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!