Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Hukumar lafiya ta bayyana yaduwar cutar Ebola a jamhuriyar Congo

Published

on

Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO), ta bayyana yaduwar cutar Ebola a Jamhuriyar Dimokiradiyar Congo a matsayin abin damuwa ga kasashen duniya.

Shugaban hukumar Tedros Adhanom Gebreyesus, ya ce, lokaci yayi da za a fadakar da duniya barazanar da cutar ke dauke da shi, kamar yadda kwamitin kwararru ya bada shawara akai.

Gebreyesus ya ce, duk da yake daukar matakin ba zai sauya asalin abinda ke faruwa a Congo ba, amma kuma zai bada damar sanar da duniya domin ganin an dauki matakan da suka dace na shawo kan cutar.

Wannan shine karo na farko da Hukumar ta dauki irin wannan mataki bayan irin wanda aka yiwa cutar murar tsintsaye a shekarar 2009 da polio a shekarar 2014 da Ebola a shekarar 2014 zuwa 2016 da kuma Zika a shekarar 2016.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!