Connect with us

Labarai

Annobar Ebola ta tilasta hana taron Jana’iza a Congo

Published

on

Hukumar lafiya ta duniya, WHO, ta ce haɗarin yaɗuwar cutar Ebola a Jamhuriyar Dimokradiyyar Kongo ya ƙaru matuƙa, sai dai ta ce babu barazana sosai kan yaɗuwar cutar a duniya.

Shugaban Hukumar Tedros Adhanom Ghebreyesus ya ce akwai bukatar a samu yarda da aminci tsakanin ma’aikatan lafiya da alummomi domin hakan zai taimaka wajen shawo kan cutar.

Hukumomi a lardin Ituri, inda cutar ta fi shafa sun haramta taron jana’iza da zaman makoki.

Hakan na zuwa ne bayan da wasu fusatattun ƴan’uwan wani mamaci suka cinna wa asibiti wuta bayan da jami’an lafiya suka ki ba su gawar ɗan’uwansu, saboda tsoron yaduwar cutar.

WHO ta ce tana tunanin mutum aƙalla 750 sun kamu da Ebola, yayin da aƙalla mutum 177 suka mutu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!