Labarai
Najeriya ta saka ido kan matafiya daga kasashen da Ebola ke yaduwa

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Najeriya, Immigration, ta tabbatar da cewa iyakokin Najeriya ba su bude haka kawai ba duk da barazanar cutar Ebola da ke yaduwa a ƙasashen Democratic Republic of the Congo da Uganda.
Kakakin hukumar, Akinsola Akinlabi, ya ce duk wanda zai shiga Najeriya ta kan iyaka sai an tantance shi tare da gabatar da takardun lafiya na ƙasa da ƙasa. Ya ƙaryata zargin cewa iyakokin ƙasar suna da rauni, yana mai cewa jami’an tsaro da fasahar zamani na sa ido a wuraren da jami’ai ba za su iya kaiwa cikin sauƙi ba.
Akinlabi ya bayyana cewa gwamnati ta samar da tsarin sa ido na zamani irin su Integrated Border Management System da Migration Information and Data Analysis System domin ƙara ƙarfafa tsaron iyaka. Ya ce gwamnati na amfani da fasaha wajen bibiyar hanyoyin shiga da fita domin rage barazanar shiga ba bisa ƙa’ida ba. Haka kuma ya tuna yadda jami’an lafiya suka yi aiki a filayen jiragen sama lokacin annobar baya, yana mai cewa za a sake ɗaukar irin waɗannan matakai idan hukumomin lafiya suka bayar da umarni.
Hukumar World Health Organization ta ayyana barkewar cutar Ebola a matsayin gaggawar lafiya ta duniya bayan cutar ta kashe kusan mutane 90 a Congo sannan ta bazu zuwa Uganda. Rahotanni sun nuna cewa zuwa ranar 19 ga Mayu an samu mutane 536 da ake zargi sun kamu, mutane 34 da aka tabbatar sun kamu, yayin da mutane 134 suka mutu. Cutar ta kai har babban birnin Congo, Kinshasa, da kuma Kampala a Uganda. Sai dai Nigeria Centre for Disease Control and Prevention ta ce har yanzu ba a samu ko mutum ɗaya da ya kamu da Ebola a Najeriya ba, yayin da Federal Airports Authority of Nigeria ta ce ta tsaurara binciken lafiyar matafiya a dukkan filayen jiragen sama na ƙasa.
You must be logged in to post a comment Login