Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Hukumar NEMA ta bukaci mutanen Kano da Jigawa su bar wuraren da ake tsammanin samun ambaliya

Published

on

Hukumar agajin gaggawa ta kasa NEMA reshen Jihar Kano, ta bukaci al’ummar jihar Kano da na Jigawa, da ke wuraren da ake fuskantar barazanar ambaliyar ruwada su tashi, don kaucewa afkuwar ta.

Wannan na kunshe ne cikin sanarwar da Shugaban gudanarwar na hukumar a nan Kano, Malam Nura Abdullahi ya sanya wa hannun.

Sanarwar ta bukaci al’ummar a jihohin biyu, su guji gina gidaje a kan hanyar ruwa, sannan su riga zubar da shara inda gwamnati ta kebe don samun saukin kwashe wa tare da kiyaye ambaliyar ruwa.

Sanarwar ta kuma ce, al’ummar su rungumi dabi’ar yashemagudanar  ruwa tare da daina zuba shara a ciki, don kaucewa mummunar ambaliyar ruwa kamar yadda ta faru a karamar hukumar Jibia na jihar Katsina.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!