Connect with us

Kiwon Lafiya

Hukumar NHIA ta kaddamar da sabon shirin gaggawa don rage mutuwar jarirai

Published

on

Hukumar Inshorar Lafiya ta Najeriya NHIA, ta kaddamar da wani sabon shiri na gaggawa domin rage mace-macen jarirai da ƙara samun damar kula da lafiyar jarirai a asibitocin gwamnati a faɗin ƙasar nan.

 

An kaddamar da wannan shirin ne a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano da ke jihar Kano, inda shugaban NHIA, Dr Kelechi Ohiri, ta ce shirin zai mayar da hankali kan jarirai da ke fuskantar matsalolin gaggawa bayan haihuwa.

 

Dakta Ohiri, wadda Dakta Salawudeen Sikiru ya wakilta, ta bayyana cewa shirin ya samo asali daga wani tsari na kulawa da lafiyar iyaye mata da aka fara fiye da shekara guda da ta gabata.

 

Jami’in ya ce  yanzu haka NHIA tana ɗaukar nauyin kuɗin magani ga jarirai a asibitocin gwamnati, inda asibitoci ke karɓar kudaden da suka kashe a kowane mako bayan an tabbatar da bayanan jinya.

 

Dakta Salawudeen Sikiru,, ya ƙara da cewa shirin ba zai tsaya kawai kan kulawar gaggawa ba, domin bayan an ceto jaririn za a yi masa rajista a kan inshorar lafiya ta ƙasa don  ci gaba da samun kulawa.

 

Shirin zai shafi iyalai marasa galihu ne kawai, tare da buƙatar lambar shaidar zama dan kasa ta NIN domin tabbatar da sahihancin rajista. 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!