Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Hukumar NYSC ta gargadi Hukumomin Jami’o’in Najeriya

Published

on

Hukumar kula da masu yiwa kasa hidima ta kasa NYSC, ta gardadi hukumomin jami’o’in kasar nan da su guji tura dalibai zuwa bautar kasa, da suka saba ka’idojin ta.

Daraktan Janar na Hukumar Birgediya Janar Shuaibu Ibrahim ne ya bayyana haka, a wani taron karawa juna sani a birnin tarayya Abuja, da ya gudana a daren jiya.

Birgediya ya kuma ce, hukumar NYSC ba zata saurara kowanne Jami’a ba, idan har ta gano suna tura dalibai zuwa bautar kasa bayan munzalin su bai kai su gudanar da hidimar kasar ba.

Ya kuam ce, hukumar a yanzu haka na shiryawa daliban jami’o’in kasar nan rukunin ’’B’’ shiga sansanonin horaswa a wayan Yunin mai kamawa, inda kuma za a ci gaba da biyan su Naira dubu Talatin a kowanne wata.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!