Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Fasinjoji 19 sun mutu sanadiyyar hatsatin mota a jihar Ondo

Published

on

Akalla mutane 19 ne suka rasa rayukansu sakamakon wani hatsarin mota da ya ritsa da su akan titin Akure zuwa Owo a jihar Ondo.

Rahotanni sun ce mutanen sun kone kurmus yadda ba za a iya gane su ba sanadiyar hadarin da ya faru a jiya Asabar.

Mai magana da yawun hukumar kiyaye abkuwar hadurra ta kasa reshen jihar Ondo, Mr. Femi Joseph, ya ce, tuni aka kai gawawwakin mutanen zuwa babban Asibitin jihar Ondo da ke garin Akure.

A cewar sa, hatsarin ya shafi wata motar safa kirar Toyota mai dauke da fasinjoji goma sha takwas, wanda ke kan hanyar zuwa Abuja da kuma wata motar dakon kaya.

Mai magana da yawun rundunar kiyaye abkuwar hadurra ta kasa reshen jihar ta Ondon, ya kuma ce, motocin biyu sun yi taho mugama ne wanda a sanadiyar haka motar safa din ta kama da wuta wanda kuma dukkannin fasinjojin da ke cikinta suka kone kurmus.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!