Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Hukuncin kotun ƙoli a shari’ar gwamnan Kano ya nuna bunƙasar dimukraɗiyya- Nasiru Garo

Published

on

Kwamishinan ma’aikatar muhalli da sauyin yanayi a jihar Kano Nasiru Sule Garo ya bayyana hukuncin kotun ƙoli a matsayin tabbatuwar shugabanci na gari a Najeriya.

Haka kuma hukuncin ya nuna ƙarara yadda aka samu bunƙaaar dimukraɗiyya a Najeriya.

Nasiru Sule Garo ya bayyana hakan ta cikin saƙon taya murna ga gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir jim kaɗan bayan yanke hukuncin da kotun ƙoli ta yi a ranar Juma’a.

Kwamishinan ya kuma ƙara da cewa, ɓangaren shari’a ya tabbatar da cewa shi ne karfin marasa ƙarfi, sannan ya buƙace su da su ci gaba da zama abin koyi domin ci gaban tsarin dimokuraɗiyyar Nijeriya.

Garo, ya kuma buƙaci magoya bayan jam’iyyar NNPP na Kano da su dage da kuma ci gaba da baiwa gwamnati goyon baya don tabbatar da manufofinta.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!