Connect with us

Labarai

IBB ya sadaukar da gidan kakanninsa don gina Asibiti a Kano

Published

on

 

Tsohon shugaban kasa Janar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB) ya bayyana kudirinsa na ci gaba da tallafawa ayyukan cigaba a fadin kasar nan. Ya bayyana haka ne yayin taron aza harsashin ginin asibiti da ya dauki nauyin ginawa a garin Kumurya, karamar hukumar Bunkure, Jihar Kano.

 

Janar Babangida wanda Janar Halliru Akilu ya wakilta, ya ce an gina asibitin ne a filin gidan kakanninsa, domin saukaka wa jama’ar yankin samun ingantacciyar kula ta lafiya.

 

A nasa jawabin, Mai Martaba Sarkin Rano, Alhaji Dr. Muhammad Isah Ummaru, wanda ya aza harsashin ginin, ya bayyana farin cikinsa da wannan gagarumin aiki da aka kawo a masarautarsa ta Rano.

 

Shi ma Dagacin Kumurya, Alhaji Salisu Musa Murabus, ya yi godiya a madadin al’ummar yankin, yayin da taron ya samu halartar Malam Ibrahim Khalil, Shugaban Majalisar Malamai ta Jihar Kano, da sauran manyan baki.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!