Connect with us

Labarai

ICPC ta hana Nasir El-Rufa’i zuwa asibiti domin a duba lafiyarsa – Muyiwa Adekeye

Published

on

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta ICPC ta hana tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufa’i, zuwa asibiti domin a duba lafiyarsa, a cewar mai magana da yawunsa, Muyiwa Adekeye.

Adekeye ya shaida wa DW Hausa cewa hukumar ta hana El-Rufa’i samun damar ganin likita duk da cewa yana fama da matsalar gani da ke buƙatar kulawar lafiya. Ya ce wannan mataki ya ƙara jefa damuwa kan yanayin lafiyar tsohon gwamnan.

Haka kuma, a watan Mayun da ya gabata, iyalan El-Rufa’i sun zargi hukumar ICPC da hana su kai masa abinci tare da takaita musu damar ganinsa. Sai dai babu wata sanarwa daga hukumar da ke tabbatarwa ko musanta waɗannan zarge-zargen.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!