Labarai
Hisbah a Kano za ta fara tantance wadanda suka nemi shiga shirin auren zawarawa

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta sanar da cewa za ta fara tantance wadanda suka nemi shiga shirin auren zawarawa daga ranar Litinin, 8 ga Yunin 2026.
Arewa Updates ta rawaito cewa, sanarwar ta fito ne ta hannun Daraktan Wayar da Kai na Hukumar, Malam Auwalu Ado Sheshe.
A cewar sanarwar, Kwamitin Shirin Auren Zawarawa na Jihar Kano karkashin jagorancin Babban Kwamandan Hisbah, Sheikh Dakta Aminu Ibrahim Daurawa, ya bukaci duk masu neman cin gajiyar shirin da su gaggauta mayar da fom dinsu domin gudanar da gwajin lafiya da sauran matakan tantancewa.
Sanarwar ta bayyana cewa masu neman shiga shirin daga kananan hukumomi za su mika fom dinsu a ofisoshin Hisbah na yankunansu.
Haka kuma, daidaikun mutane da kungiyoyi za su kai fom dinsu zuwa Hukumar Yaƙi da Cutar Kanjamau ta Jihar Kano da ke Na’ibawa, inda za a fara tantance su daga karfe 8:00 na safe ranar Litinin.
You must be logged in to post a comment Login