Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

ilimi

Ilimi: Jigawa ta ɗauki nauyin ɗalibai zuwa ƙaro karatu a Sudan

Published

on

Gwamnan jihar Jigawa Muhammadu Badaru Abubakar ya dauki nauyin ɗalibai 210 zuwa Sudan don ƙaro karatu kan aikin likitanci.

Mataimakin gwamnan, Alhaji Umar Namadi ne ya bayyana haka lokacin da shugaban ƙungiyar Editocin Najeriya, Mustapha Isah da mambobin kwamitin suka kai masa ziyarar ban girma a Dutse.

Namadi ya ce manufar ɗaukar nauyin ɗaliban shi ne, cike giɓin da ke akwai a ɓangaren kiwon lafiya.

Ya ce, ana sa ran ɗaliban bayan kammala karatunsu za su yi aiki a yankunansu don taimakawa harkokin lafiya a jihar, musamman ma yankunan karkara.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!