Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Jigawa

An rantsar da sabbin shugabannin ƙungiyar ICAN na Kano da Jigawa

Published

on

Gwamatin jihar Jigawa ta yi kira ga sabbin shugabannin ƙungiyar akantoci ta ƙasa reshen jihar Kano da Jigawa (ICAN) da su yi aiki tuƙuru tare da fito da tsare-tsaren da za su ciyar da ƙungiyar gaba.

Mataimakin gwamnan jihar Alhaji Umar Namadi ne ya bayyana hakan yayin bikin rantsar da sabbin shugabannin ƙungiyar karo na talatin da tara da aka gudanar a nan jihar Kano.

Ya ƙara da cewa lokaci yayi da sabbin shugabannin za su mayar da hankali wajen wayar da kan ƴan kasuwa matsakaita da ƙanana don sanin muhimmancin ilimin akantanci tare da amfana dashi.

Namadi ya kuma yabawa ƙungiyar ta ICAN musamman wajen yadda take bai wa gwamnatoci shawara kan yadda za su magance matsalar tattalin arziki.

A nasa ɓangaren sabon shugaban ƙungiyar Dakta Abubakar Umar Farouk cewa yayi abin takaici ne yadda ake samun ƙarancin masu rubuta jarabawar zama ƙwararrun akantoci a ƙungiyar daga arewacin kasar nan.

Dakta Abubakar Umar ya kuma ce akwai mutanen da a shirye suke su ɗauki nauyin waɗanda za su rubuta jarabawar ƙungiyar sai dai rashin sani yasa da yawa al’ummar arewacin kasar nan na rasa damar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!