Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ina da nagartar da zan tsaya takarar shugaban ƙasa a 2023 – Yahaya Bello

Published

on

Gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello ya ce, yana da duukanin nagartar da zai iya tsayawa takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2023.

Yahaya Bello ya sanar da hakan yayin da ake hira da shi ta cikin wani shiri a gidan talabijin na Arise ranar Litinin.

Ya ce, a shirye yake ya karɓi ragamar shugabancin ƙasar nan daga hannun shugaba Muhammadu Buhari la’akari da kyakyawan rahoton da yake da shi a jihar ta Kogi.

“In sha Allah za a rantsar da ni a shekarar 2023 a matsayin zaɓaɓɓen shugaban ƙasa, wanda zan karɓa daga hannun Buhari a ranar 29 ga watan Mayun 2023”.

“Zan fitar da Najeriya daga cikin halin ƙuncin da ta ke ciki da zarar na ɗare bisa karagar mulkin shugabancin ƙasa, musamman ma ayyukan ta’addanci, kuma wannan amsa kiraye-kirayen al’umma ne na buƙatar na tsaya takarar shugaban ƙasa” a cewar Yahaya Bello.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!