Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Siyasa

Yan takarar shugaban kasar Najeriya za su tafka muhawara ranar 19 Janairun badi

Published

on

Kungiyar shirya muhawara kan siyasa ta kasa ta ware ranar 19 ga watan Janairun shekarar 2019 a matsayin ranar da ‘yan takarar shugabancin kasar nan da suka tsaya karkashin inuwar jam’iyyu daban-daban za su gudanar da mahawara.

Haka zalika kungiyar ta kuma ware ranar 14 ga watan Disambar bana a matsayin ranar da mataimakan ‘yan takarar shugabancin kasa kuma za su gudanar da ta su muhawarar.

Shugaban kungiyar Mr. John Momoh ne ya bayyana hakan, lokacin da yake jawabi yayin wani taron manema labarai yau Alhamis a birnin tarayya Abuja.

Mr. Momoh wanda shi ne shugaban kungiyar kafafen yada labarai na rediyo da talibijin na Najeriya, ya ce, taron muhawarar za a gudanar da shi ne a dakin taro na Transcorp da ke Abuja, kuma za a nuna shi tare da sanya muryoyin su kai tsaye a gidajen talibiji da rediyo da ke karkashin shugabancin kungiyar a fadin Najeriya.

Ana sa ran shugaban kasa Muhammadu Buhari da ya sake tsayawa takarar shugaban kasa karkashin inuwar jami’iyyar APC da Atiku Abubakar na babbar jam’iyyar adawa ta PDP za su halarci taron muhawarar.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!