Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

KannyWood

Ina so na zama ‘yar kasuwa kamar Dangote –Sadiya Kabala

Published

on

Jarumar fina-finan Hausa Sadiya Kabala ta bayyana cewa burinta shi ne ta zama ‘yar kasuwa mai kudi kamar Alhaji Aliko Dangote.

Sadiya Kabala ta wallafa a shafinta na Instagram cewa ”Mafarki na shi ne in zama ‘yar kasuwa kamar Dangote nima wata kila a kirani ‘Yargote”

Wannan batu na jurumar dai ya sanya cecekuce tsakanin mabiyanta, wadanda suka rika bayyana mabam-bamtan ra’ayoyi akai, yayin da wasu ke mata fatan alkhairi, wasu kuwa tuni ma suka fara kiranta da ‘Yargote.

Wannan dai ba shi ne karon farko da jaruman masana’antar Kannywood ke fatan zamowa ‘yan kasuwa ba, domin kuwa ko a baya-bayan nan matashiyar jaruma Maryam Yahya ta bude shagon kasuwanci a Kano.

Haka kuma ko a makon da ya gabata a wata tattaunawa da jarumi Ali Nuhu yayi da sashen hausa na BBC ya bayyana cewar shi ma yana hadawa da wasu sana’o’in baya ga harkar sa ta wasan kwaikwayo.

Labarai masu alaka:

Ina fatan Allah ya bani sana’ar da tafi Kannywood -Mansur Makeup

Ni da Ali Nuhu laifunmu ne ke haifar da matsala a Kannywood –Adam Zango

Jaruman Kannywood sun fara bayyana da Iphone 11

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!