Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kaduna

Inconclusive: An shiga ruɗani a Kaduna bayan hukuncin kotu

Published

on

Rahotanni na nuna cewa an shiga ruɗani a jihar Kaduna bayan sanar da hukuncin Kotu kan zaɓen gwamna.

Freedom Radio Kaduna ta tawaito cewa, a halin yanzu dukkanin ɓangarorin na gudanar da shagulgulan murna a matsayin sune suke da nasara.

Kazalika a ɓangaren lauyoyin da ke kare ɓangarorin biyu sun shiga ruɗani bisa rashin takamaiman hukuncin da aka dogara a kan sa.

Sai dai lauyan jam’iyyar PDP Barista Baba Lawal Aminu ya ce “A kotun alƙalai uku ne a ciki, biyu daga ciki suka bada umarnin aje a sake zaɓe a mazaɓun da ake zargin an samu maguɗi, yayin da alƙali ɗaya ya ce ya tabbatar da gwamna mai ci a matsayin wanda ya samu nasara, saboda haka ita Shari’a majority wato mafi rinjaye ake tafiya a kanta.”

A bangaren lauyan jam’iyyar APC Barista Sunusi Musa kuwa ya ce “Kotu ta kori ƙarar gaba ɗaya daga gabanta sakamakon rashin gamsassun hujjoji da jam’iyyar PDP ta gabatar, don haka yanzu ba batun sake zaɓe har sai in jam’iyyar PDPn da ɗaukaka ƙara.

Wannan ne ya nuna cewa akwai ruɗani game da hukuncin da aka yanke, sakamakon yadda ɓangarorin biyu ke ganin sune da nasara, a gefe guda kuma magoya bayan su na ci gaba da murna.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!