Connect with us

Labarai

INEC na shirin fara rajistar masu kaɗa ƙuri’a a Dala

Published

on

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa, INEC, ta sanar da cewa za ta fara rajistar masu kaɗa ƙuri’a a dukkanin yankuna na Ƙaramar Hukumar Dala, daga ranar 2 ga watan Fabrairu.

 

Jami’in Zaɓe na Ƙaramar Hukumar Dala, Alhaji A. A. Maulud, ne ya bayyana hakan yayin wani taron masu ruwa da tsaki kan harkokin zaɓe da aka gudanar a yankin.

 

A cewar sanarwar, da jami’ar yada labaran ta karamar hukumar Dala ta fitar Hassana Aminu, ta ce rajistar za ta shafi dukkan mutanen da suka cancanta amma ba su da Katin Zaɓe na Dindindin.

 

Haka kuma, aikin zai bai wa waɗanda katin zaɓensu ya lalace, ko ke da kuskure a bayanansu, da kuma waɗanda ke son canja wurin rajistarsu zuwa wata rumfar zaɓe ko jiha da suka zaune, damar yin gyara.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!