Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kano:An harbe mutane biyu tare da garkuwa da wani dan kasar Lebanon

Published

on

Masu garkuwa  da mutune sun harbe mutane biyu inda kuma suka yi garkuwa da wani dan kasar Lebanon ma’aikacin kamfanin Triacta dake aikin gina gadar dangi.

Lamarin dai ya faru ne da safiyar yau talata inda ake zargin masu garkuwa da mutanen sun zo a wata mota kirar golf da misalig karfe bakwai na safiyar yau talata suka kuma harbin iska don tarwatsa jama’a.

Wasu shaidun gani da ido sun shaidawa wakilinmu Abba Isah Muhammad, cewa saida masu garkuwa da mutanen suka harbe ma’aikatan kamfanin biyu kafin dauke Mr Yalla Yaba wanda shi ma’aikacin da ake zargin anyi garkuwa da shi.

Sai dai koda muka tuntubi kakakin rundunar Yan Sandan jihar Kano DSP Abdullahi Haruna, ta wayar hannu ya ce sun samu labarin faruwar lamarin kuma suna jiran bayanin baturen Yan sadan yanki da abun ya faru.

Wakilinmu Abba Isah Muhammad, da ya halarci gurin da lamarin ya faru ya ruwaito cewa alamuran aikin ya tsaya cik bayan faruwar lamarin.

=

AIM

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!