Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Hukumar INEC ta dakatar da jami’an ta 205 da aikata wasu laifuka

Published

on

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta dakatar da wasu jami’an ta 205, sakamakon aikata laifuka daban-daban yayin zaben shekarar 2015.

Shugaban hukumar na kasa farfesa Mahmud Yakubu ne ya bayyana hakan, lokacin da yake jawabi yayin taron wani kwamitin mai zaman kan sa da ke sanya ido kan yadda ake gudanar da ayyuka da aka gudanar a Abuja.

Shugaban hukumar ya bayyana cewa hanawa da nadawa, hadi da karin girma da kuma tsawatarwa da hukumar take aiwatarwa ya kai matakin da ake bukata.

Farfesa Mahmud Yakubu ya kara da cewa irin korafin da hukumar take samu daga al’ummar kasar nan, ya taimaka mata wajen cimma manufofi da dama, musamman ma wajen tabbatar da sahihancin zabe.

Yace yanzu haka hukumar na cigaba da gudanar da ayyukan tunkarar babban zaben shekarar 2019, tare da cewa akwai bukatar hukumar ta zabo gogaggun ma’aikatan da zasu yi mata aikin zaben na shekarar badi.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!