Connect with us

Ƙetare

Isra’ila ta ci gaba da kai hare-hare Gaza duk da yarjejeniyar tsagaita wuta

Published

on

Ma’aikatar lafiya ta Gaza ta  ce, hare-hare ta sama da Isra’ila ke kai wa sun kashe mutum biyar a kudancin Zirin, tare da jikkata wasu da dama.

Waɗan da suka ga harin a sansanin ‘yan gudun hijira na al-Mawasi sun ce Isra’ilar ta kai harin ne kan wani tanti.

Haka zalika sun tabbatar da cewa ta  sake  biyo baya da wasu hare-haren a kusa da asibitin Kuwait, abin da ya dugunzuma iyalan da ke fake a wajen.

Hamas ta kira harin da dabbanci – na kan-mai-uwa-da-wabi, wanda kuma ya saɓa da yarjejeniyar dakatar da buɗe wuta da Amurka ta samar- da ta fara aiki makwanni  bakwai da suka  wuce.

Rundunar sojin Isra’ilar ta ce ta kai harin ne a matsayin martani bayan da aka farmaki dakarunta.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!