Ƙetare
Isra’ila ta sake kai sabbin hare-hare a Lebanon

Sojojin Israel sun kai hari ta sama kan wani ginin gidaje da ke tsakiyar birnin Beirut a ƙasar Lebanon, a wani sabon hari da aka kai yayin da rikicin Gabas ta Tsakiya ke ci gaba da ƙamari. Rahotanni sun ce harin ya auku ne a unguwar Aisha Bakkar, wadda ke kusa da babbar cibiyar kasuwanci a birnin, inda aka ga wuta da hayaki suna tashi daga ginin bayan harin.
Rahotanni sun ce wannan shi ne karo na biyu da Isra’ila ke kai hari a tsakiyar Beirut tun bayan da rikici ya ƙara tsananta a yankin. Rikicin ya ƙara kamari ne bayan ƙungiyar Hezbollah ta kai hari kan Isra’ila a matsayin martani ga kisan jagoran addinin Iran Ayatollah Ali Khamenei a hare-haren haɗin gwiwar Amurka da Isra’ila.
A halin da ake ciki, hukumomin Lebanon sun ce sama da mutane 759,000 sun rasa matsugunansu sakamakon hare-haren da ake ci gaba da kai wa a sassan ƙasar, yayin da jami’an agajin gaggawa ke ci gaba da kwashe waɗanda suka jikkata.
Rahotanni sun kuma nuna cewa an kai wasu hare-hare a kudancin Lebanon da suka yi sanadin mutuwa da jikkatar wasu mutane.
You must be logged in to post a comment Login