Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

ISWAP ta rabawa jama’a kudade a Borno

Published

on

Rahotanni daga jihar Borno sun tabbatar da cewa ‘yan ta’addar ISWAP sun raba wa jama’a makudan kudade a kan hanyar Maiduguri zuwa Monguno na jihar dake a yankin Tafkin Chadi.

Rabon kudin dai na zuwa ne bayan babban bankin kasa CBN ya tsawaita wa’adin ci gaba da amfani da tsaffin kudade zuwa Kwanaki 10.

An tabbatar da cewar ‘yan ta’addar sun tsaya akan titi dauke da buhunhunan tsaffin kudin da suka kunshi Naira 200 da 500 da kuma 1000 suna rarrabawa matafiyan da ke a kan hanyar.

Shaidun gani da Ido sun bayyanawa cewar ‘yan ISWAP din da suka yi shigar kayan Sojoji tare da girke motocin sulke guda 2 akan hanyar inda suke tare motocin suna bin fasinjojin daya bayan daya da kyautar tsaffin kudin a babbar hanyar da ke karamar hukumar Guzamala.

Guda daga cikin fasinjan da ya riski rabon kudin ya shaidawa manema labarai cewa mayakan na ISWAP sun baiwa kowanne fasinja da ke cikin motar kudin da yawansu ya kai dubu 100.

Rahoto: Aminu Halilu Tudun Wada

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!