Connect with us

Labarai

JAMB ta umarci jami’o’i su gaggauta kammala daukar ɗaliban bana

Published

on

Hukumar Shirya Jarabawar Shiga manyan makarantun gaba da sakandare ta kasa JAMB ta umarci jami’o’in gwamnati da su gaggauta kammala daukar ɗalibai na shekarar 2025 kafin ranar 31 ga Oktoban bana.

 

A jadawalin da hukumar ta fitar, tace jami’o’i masu zaman kansu suma wajibi ne su kammala daukar ɗalibai kafin 30 ga Nuwamban shekarar nan, yayin da aka ba dukkanin manyan makarantu na gaba da sakandare – na gwamnati ko na ƙasa masu zaman kansu – wa’adin zuwa ƙarshen shekara.

 

JAMB ta ce hakan yana cikin jadawalin da aka amince da shi a taron da aka gudanar na tsare-tsaren ilimi a shekarar nan bisa jagorancin ministan Ilimi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!