Connect with us

Labarai

JAMB ta yi hasashen samun kuɗaɗen shiga har fiye da naira biliyan 23 a bana

Published

on

Hukumar shirya jarabawar shiga manyan makarantu ta Najeriya,  JAMB, ta yi hasashen samun kuɗaɗen shiga watau IGR har naira biliyan 23 da miliyan 800 a shekarar nan da muke ciki ta 2026.

 

Hukumar ta ce hasashen  ya biyo bayan ƙaruwa da yawan masu rubuta jarabawar shiga jami’o’i ta UTME, tare da matakan da ake ɗauka na inganta tsarin tattara kuɗaɗe da gudanar da jarabawa cikin gaskiya da tsari.

 

Haka kuma, JAMB ta sanar da shirinta faɗaɗa cibiyoyin rubuta jarabawar UTME a faɗin Najeriya, inda ake sa ran ƙara yawan cibiyoyin daga adadin da ake da su yanzu zuwa 1,000.

Hukumar, a ta kara da cewa, hakan wani mataki ne na rage cunkoso da sauƙaƙa wa ɗalibai tafiye-tafiye masu nisa da kuma bai wa kowa damar rubuta jarabawar cikin yanayi mai kyau.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!