Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Hukumar JAMB: Dalibai 869,709 ne suka yi rijista don jarabawar watan Maris

Published

on

Hukumar shirya jarabawar shiga makarantun gaba da Sakandire ta kasa (JAMB) ta ce dalibai dubu dari takwas da sittin da tara da dari bakwai da tara ne suka yi rajista domin rubuta jarabawar wannan shekara da za a yi a watan Maris.

Hakan na kunshe ne cikin rahoton da hukumar ke fitarwa a mujallarta na mako-mako.

Hukumar ta JAMB ta kuma ce ta soke wasu cibiyoyin rubuta jarrabawar guda tara sakamak on karya ka’idoji da su ka yi.

Rahoton na hukumar JAMB ya kara da cewa, cibiyoyin da aka soke lasisin su, sun bukaci kudade fiye da adadin da gwamnati ta ayyana.

Haka kuma hukumar JAMB ta ce ana ci gaba da binciken wasu cibiyoyi guda goma da ke jihohin Lagos da Filato.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!