Connect with us

Labarai

Jami’an Indonesia da Thailand sun fara aikin zakulo mutanen da Ambaliya ta hallaka

Published

on

Hukumomin Indonesia da Thailand sun fara aikin share tarkace domin lalubo ɗaruruwan mutanen da har yanzu ba a gani ba, bayan ambaliyar ruwa da zaftarewar ƙasa da ya kashe aƙalla mutum 480 a kudu maso gabashin Asiya. Ruwan sama mai ƙarfi ya mamaye yankunan Indonesia, Thailand da Malaysia a makon da mukai bankawana da shi, wanda ya bar dubban mutane a maƙale ba tare da mafaka ko kayan agaji ba.

Adadin waɗanda suka mutu a Indonesia ya ƙaru zuwa 316, yayin da 289 har yanzu ba a kai ga gano su ba, a cewar sabbin alƙaluman da hukumar jin ƙai ta ƙasar ta fitar.

A Thailand, bayanai sun tabbatar da cewa, aƙalla mutane 162 ne suka mutu, inda hukumomin da abin ya shafa ke ci gaba da aikin lalube.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!