Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Jami’an Kwastam sun cafke makamai a tashar ruwan Ikko

Published

on

Jami’an hukumar yaki da fasa kwauri ta Nijeriya Kwastam, sun samu nasarar cafke wasu makamai da harsasai a tashar ruwan Lagos da ake zargin an shigo da su ne ta ɓarauniyar hanya.

Wani babban jami’in hukumar ya bayyana cewa sauran kayan da da hukumar ta gano sun haɗa da kakin sojoji da kuma miyagun kwayoyi.

Haka kuma ya kara da cewa makaman sun haɗa da bindigogi masu sarrafa kansu da kuma samfurin harba ka ruga.

Hukumar ta ce ta samu nasarar kwato kayayyakin ne yayin da ake duba kayayyakin da aka shigo da su cikin ƙasar.

BBC ta ruwaito cewa, Sai dai babu wasu bayanai na cewa ko an kama wasu da ke da alaka da kayan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!