Connect with us

Labarai

Jami’an tsaron Chadi sun kama ɗan shugaban Boko Haram Mohammed Yusuf

Published

on

Hukumomi a ƙasar Chadi sun kama dan shugaban ƙungiyar Boko Haram na farko a ƙasar Chadi mai suna Muslim Mohammed Yusuf.

An kama Musulim ne tare da wasu mutum biyar da ake zargin ƴan Boko Haram ne, ƙungiyar da mahaifinsa ya assasa a kasar nan a shekarun baya.

Rundunar ƴansandan Chadi ta tabbatar da kama ƴan Boko Haram shida, amma ba ta iya tantance ɗan Muhammad Yusuf a ciki ba, kamar yadda gidan Talabijin na Channels ya ruwaito.

Sai dai wata majiyar tsaro da kafar AFP ta zanta da su, sun tabbatar mata da kama ƴan Boko Haram shida, ciki har da shi Muslim ɗin.

An fi sanin Muslim da suna Abdrahman Mahamat Abdoulaye, kuma ƙani ne ga jagoran ISWAP Habib Yusuf, wanda aka fi sani da Abu Mus’ab Al-Barnawi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!