Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Jami’ar Yusuf Maitama Sule zata yi bikin yaye dalibai

Published

on

Jami’ar Yusuf Maitama Sule da ke nan Kano, ta ce za ta yi bikin yaye dalibai dubu biyu da dari biyar da goma sha hudu a jibi Asabar din karshen makon nan.

Bikin yaye daliban dai ya hada da dalibai da suka kammala karatu a jamiar daga shekarar 2016 da 2017 da kuma 2018.

Shugaban jami’ar ta Yusuf Maitama Sule Farfesa Mustapha Ahmad Isa ne ya bayyana hakan yayin zantawa da jaridar Solacebase anan Kano.

Farfesa Mustapha Ahmad Isa ya kara da cewa, daliban da suka kammala jami’ar a bana ba za su shiga cikin bikin ba, kasancewar sun kammala jami’ar ne bada dadewa ba, ga kuma rashin fitowar sakamakon jarrabawa
karshe akan lokaci su na

Mustapha Ahmad Isa wanda Farfesa ne a bangaren turanci da kimiyyar harshe, ya ce jamiar ba za ta bada digirin girmamawa ba.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!