Connect with us

Labarai

Jam’iyyar PDP na ci gaba da shirye-shiryen gudanar da babban taron ta na kasa

Published

on

Jam’iyyar PDP a Najeriya ta ci gaba da shirye-shiryen gudanar da babban taron ta na ƙasa a Ibadan duk da sabon hukuncin kotuna da rikice-rikicen cikin gida. 

 

An tsara taron ne domin gudana shi a ranar 15 da 16 ga watan da muke ciki na Nuwamba.

 

A makon da ya gabata, Kotun Jihar Oyo ta bawa jam’iyyar damar cigaba da shirin taron. 

 

Sai dai daga baya wata kotu a Abuja ta bayar da umarnin dakatar da shi tare da hana INEC halarta ko amincewa da duk wani abu da ya shafi taron, wanda hakan ya jefa jam’iyyar cikin rudani.

 

Wani sashe na jam’iyyar da Sam Anyanwu ke jagoranta ya sanar da dage taron, amma shugabancin jam’iyyar na Umar Damagum ya musanta hakan, yana mai cewa babu wani hukuncin kotu da ya isa ya dakatar da shirye-shiryen.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!