Connect with us

Jigawa

Jigawa: Ƴan sanda sun cafke matashin da ake zargi da kashe mahaifinsa

Published

on

Rundunar ƴan sandan jihar Jigawa, ta kama wani matashi mai shekaru 26 da take zarginsa da hallaka mahaifinsa ta hanyar sassarashi da makami.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar SP  Lawan Shisu Adam, ne ya shaida wa Freedom Radio hakan.

Ya ce, lamarin ya afku ne a garin Sara da ke yankin karamar hukumar Gwaram ta jihar.

Haka kuma, ya ƙara da cewa za su gurfana da matashin da zarar sun kammala bincike.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!