Connect with us

Labarai

Jigawa: Ma’aikatu da Hukumomi sun fara kare kasafinsu na badi a Majalisar dokoki

Published

on

Ma’aikatu da Hukumomin Gwamnatin jihar Jigawa sun fara ziyartar kwamitocin Majalisar dokoki domin kare kasafin kudinsu na badi bayan Gwamna Malam Umar Namadi ya gabatarwa da zauren majalisar kunshin kasafin kudin a satin Daya gabata.

Kwamitin Kudi na Majalisar Karkashin Jagorancin Lawan Muhammad Dansure shine ya bude fara kare Kasafin kudin inda Hukumomin dake Karkashin Ma’aikatar Kudi kamar Hukumar tattara Kudaden shiga ta jiha da Ofishin babban Akanta suka bi Sahu.

Haka kuma kwamitin dake Kula da ayyuka na musamman da kwamitin Kula da bada agajin gaggawa sun gurfana a gaban kwamitocin dake karkashinsu.

Wakilin Freedom Radio a majalisar dokokin ta Jigawa, ya ruwaito cewa, yayin tantance Kasafin kudin kwamitocin Majalisar zasu bukaci bayanai daga bangaren Ma’aikatu da Hukumomin Gwamnatin kan yadda zasu kashe Kudaden da aka ware musu a kunshin kasafin kudin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!